wanna shafi yana zuwa muku kai tsaye daga masallacin jumu'a Jami'u Abu hurairah Dake kurna y'an kifi titin y'an smogal a karamar hukumar dala dake kano Nigeria kar kashin jagorancin Sheik Muhammad Sani Uthman Kurna
JERIN SUNAYEN MATAN DA YA HALATTA MUTUM MUSULMI YA YA AURAE
SU NE KAMAR HAKA:-
1.Diyar mijin mahaifiya wacce ta haifeka
2.Diyar mijin mahaifiya wacce ta shayar da kai nono
3.Matar mijin mahaifiya wacce ta haifeka(in sun rabu)
4.Matar mijin mahaifiya wacce ta shayar da kai nono (in sun rabu)
5.Uwar mijin mahaifiya wacce ta shayar da kai
6.Uwar mijin mahaifiya wacce ta shayar da kai nono
7.Diyar mijin diyar wacce ka haifa
8.Diyar mijin diyarka ta shayarwa
9.Uwar matar danka wadda ka haifa
10.Uwar matar danka na shayarwa
11.Diyar matar danka wadda ta wani miji
12.Diyar matar danka na shayarwa
13.Uwar matar babanka mahaifi
14.Uwar matar babanka na shayarwa
15.Matar dan matarka na cikinta(in sun rabu)
16.Matar dan matarka na shayarwa(in sun rabu)
17.Yar'uwar yar'uwarka wacce kuka hadaa uwa daya da ita,ta hanyar nasaba ko shayarwa
18.Yar'uwar dan'uwanka wadda kuka hada uwa daya da shi
19.Yar'uwar shayarwar dan'uwanka na wata macen daban
20.Yar'uwarka ta shayarwa ta halatta ga dan'uwanka na nasaba
21.Idan wata macen daban ta shayar da yar'uwarka ko dan'uwanka nono,to kai ya halatta ka aureta
22.idan wata mace daban ta shayar da dan'danka nono,to kai ya hakatta ka aureta
23.Idan wata macen daban ta shsyar da dan cikinka nono,to kai ya halatta ka aurota
24.Idan wata mace daban ta shayar da danka nono,to kai ya halatta ka aurota
25.Idan wata mace daban ta shayar da danka,to kai ya halatta ja auri matar
26.Idan wata mace daban ta shayar da kawunka ko gwaggonka nono,to kai ya hakatta ka aureta
27.Idan wata mace daban ta shayar baffanka ko innanka wato yar'uwarsa,to kai ya halatta ka aureta
28.Uwar jikanka na shayarwa ya halatta ka aureta
29.Ya halatta ka auri kakar jaikanka na shayarwa
30.Ya halatta ka auri jajar danka na shayarwa
31.Ya halatta ka auri kakar danka na shayarwa
32.Ya halatta ka auri gwaggon danka na shayarwa
33.Ya hakatta ka auri mata majin diyarka
34.Ya halatta ka auri matar gwaggon danka na shayarwa
35.Ya halatta mace ta baban dan'uwanta na shayarwa
36.Ya halatta mace ta auri,uban jikanta na shayarwa
37.Ya halatta mace ta auri,jakan jikanta na shayarwa
38.Ya halatta ka auri,kakar danka na shayarwa
39.Ya hakatta ka auri,uwar matar da ta shayar da danka
40.Ya halatta ka auri,diyar matar da ta shayar da danka
41.Ya halatta ka auri,diyar matar da ta shayar da dan'dan uwanka ko yar'uwarka
42.aYa halatta ka auri,matar da ta shayar da jikarka
43.Ya halatta ka auri,matar kakanka wadda kuke ciki daya ko uba daya ko uwa daya ko da yana da rai,haka shima zai iya aurar taka ko kana da rai kaima(Indai auren na baya ya rabu)
44.Ya halatta ka auri,matar wan babanka ko yana da rai(in sun rabu)
45.Ya hakatta ka auri,matar dan'uwan babarka koda yana da rai(in sun rabu)
WADANNAN SU NE JERIN GWANON MATAN DA YA HALATTA,MUSULMI YA AURA.
ALLAH SHI NE MASANI.
DAGA
DAN'UWANKU
ABDULMAJID IBN NUHU
DA MASU TAIMAKAMIN
MALAM ADAMU KABIRU YARGAYA
MALAM AWAISU AL'ARABEE FAGGE
MALAM SANI USMAN KURNA
MALAM DR. JAMILU ZAREWA
MALAM BASHIR JOURNALIST
MALAM NAZIFI KABIRU
MALAM AHMAD IBN TAIMIYYAH
DA SAURAN MALAMAI WADANDA,BAZA SU IRGU ANAN BA
DA KU MASU BIBIYATA
ALLAH YA SAKAWA KOWA DA AKKHAIRI,YA KARA MANA IKLASI,AMIN.
MATAN DA MUSULUNCI YA HANA KA,KA AURA DA KUMA WADANDA YA YARDA KA AURA.
An karbo daga Ummu habibata R.A yar abu sufyan R.A cewa "YA MA'AIKIN ALLAH SAW mai zai hana ka auri yar'uwata diyar abu sufyan mana?"
sai MANZON ALLAH S.A.W yace da ita "YANZU KINA SON HAKA?"
sai na ce da shi S.A.W "ee zan so hakan mana tunda ni nasan ba zai yiwu na zauna da kai ni kadai ba,don haka haka kuwa duk wani wanda zai yi tarayya dani a kanka,ai na fi son yar'uwata ta yi tarayya dani(a kanka).
BUKHARI ya rawaito shi a hadisi mai lamba 5101/43/9 ,5106,5107,5123
MUSLIM ya rawaito shi a hadaisi mai lamba ta 26,25,10,4
Su matan da aka haramtawa musulmi ya aura sun kasu kashi kashi NA FARKO sun haramta ya aure su har abada,NA BIYU kuma sun haramta ya auresu ne na wani lokaci.
KASHI NA FARKO
WADANDA SUKA HARAMTA A AURESU HAR ABADA,SU NE KAMAR HAKA:-
1.Uwar mahaifiya da mahaifiyarta har ya zuwa ba iyaka.
2.Yar'tsatso da diyarta da itama diyar har ya zuwa ba iyaka.
3.Yar'uwa shakikiya
4.Yar'uwa li'abbiya.
5.Yar'uwa li'ummiya
6.Yar yar'uwa
7.Yar yar'uwarka wadda kuke uba daya
8.Yar yar'uwa wadda kuke uwa daya
9.Yar dan'uwanka shakiki
10.Yar dan'uwanka wanda kuke uba daya
11.Yar dan'uwanka wanda kuke uwa daya
12.Kanwar babanka shakikiya
13.Yar mahaifi shakikiya
14.Yar%mahaifi wacce suke uba daya
15.Yar'mahaifi wacce suke uaw daya
16.Yar'uwar mahafiyarka shakikiya
17.Yar'uwar mahaifiyarka wacce suke uba daya
18.Yar'uwar mahaifiyarka wacce suke uwa daya
19.Mahaifiyar matarka
20.Kakar matarka har zuwa ba iyaka
21.Diyar matarka(agola)
22.Jikar matarka(diyar yar'ka,wato agolarka)
23.Matar mahaifinka
24.Matar kakanka(na wajen uwa ko uba)
25.Matar danka na cikinka
26.Matar jikanka komai nisansa
27.Diyar yar'ka(jikarka)
28.Jikar yarka duk nisanta
29.Babarka ta shayarwa
30.Kakarka ta shayarwa
31.Yarka ta shayarwa
32.Kanwarka ta shayarwa
33.Diyarka ta shayarwA
34.Jikarka ta shsyarwa
35.Gwaggonka ta shayarwa
36.innarka ta shayarwa
37.Matar da akwai aure a kanta(matar wani)
WADANNAN SUNE MATAN DA SUKA HARAMTA A GAREKA KA AURE SU,HARAMCI NA HAR ABADA.
KASHI NA BIYU
AMMA SU KUWA MATAN DA YA HARAMTA KA AURE SU NA WANI LOKACI SU NE KAMAR HAKA:-
1.Yar'uwar matarka da kuke tare da ita
2.Innar matarka da kuke tare da ita
3.Gwaggon matarka da kuke tare da ita
4.Matar da ake son a aura kafin mace ta hudu 4 da aka saka ta gama iddah
5.Mazinaciya har sai ta tuba
6.Matar da aka saka saki uku ko sau uku har sai tayi wani auren
7.Matar da ta yi haramar ga hajji ko umara har sai ta kammala
8.Mai iddar wani har sai ta gama
WADANNA. SU NE MATAN DA YA HARAMTA A AURE SU NA WANI LOKACI NA WANI LOKACI.
MATAN DA YA HALATTA MUSULM YA AURA.
ALLHA YASA MUDA CAI NAN GA BA ZA MU KAWO MUKU MATAN DA YA HA LARTA KU AURA.